Yan bindiga sun kashe ƴan sanda uku a jihar Kwara

An kashe jami’an yan sandan kwantar da tarzoma su akalla  uku tare da jikkata wasu biyu a wani farmaki da yan bindiga su ka kai a sansaninsu dake Tenebo a karamar hukumar Kaiama  ta jihar Kwara.

Harin da ya shammaci jami’an tsaron an kai shi ne da tsakar daren ranar Asabar.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun farma sansanin su da yawa a yayin da  wasunsu suke akan babura.

Muhammad Abdul dake zaune a garin ya bayyana cewa maharan masu yawa sun kai farmakin ne da ƙarfe 02:00 na dare inda su ka yi ƙoƙarin kutsawa garin amma sai suka fuskanci turjiya daga jami’an tsaro abun da  ya jawo aka ɗauki sa’o’i ana musayar wuta da su.

“Bayan fafatawar ne aka kashe ƴan sanda uku tare da jikkata wasu biyu. Daga nan yan bindigar suka juya amma babu wanda aka yi garkuwa da shi.Amma kuma bamu da masaniya na kisan wasu daga cikin maharan,” ya ce.

Shima wani mazaunin garin mai suna, Halidu Umar ya ce dukkansu da suke da gidajen ta wajejen yankin basu iya samu sunyi bacci  ba saboda fargaba.

Kwamishinan yan sandan jihar,  Adekimi Ojo ya ya tabbatar da kai harin a zantawar da ya yi ta waya da wakilin jaridar Daily Trust.

More from this stream

Recomended