Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi.

A cewar mazauna ƙauyen gungun ƴan fashin daji da yawansu ya kai 50 sun kai farmaki garin a ranar Juma’a inda suka riƙa harbin kan me uwa da wabi ta ko ina kafin daga bisani maharan su janye ya zuwa cikin daji sai da  kashe mutanen garin  su 7.

Dagacin ƙauyen Tudun Bici Alhaji Muhammad Mikailu lokacin da yake bayyana halin da suke ciki ga gwamnan jihar Nasir Idris lokacin da ya kai ziyara garin ya roƙe shi da ya tura ƙarin jami’an tsaro ya zuwa garin domin kare faruwar hari makamancin haka anan gaba.

A yayin da yake jajantawa dagacin kan mutuwar mutane 7 a ƙauyen gwamnan ya bada tabbacin cewa za a  tura ƙarin jami’an tsaro zuwa Tudun Bici domin kare mutane da dukikoyinsu daga fuskantar hare-hare.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...