Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen Ɗan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen ɗan fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar Najeriya da Nijar.

Kachalla Mai Daji ya kashe mutane da dama tare da ƙona ƙauyuka masu yawa yin garkuwa da mutane tare da sakawa ƙauyuka haraji.

Ya yi ƙaurin suna wajen addabar ƙauyukan da suke gabashin garin na Illela irinsu Tozai, Sabon Garin Darna, Darna Tsolawo, Tudun Gudali, Basanta, Dankadu, Takalmawa, Gidan Hamma, Ambarura, Gidan Bulutu dama wasu ƙauyuka da dama.

Sojojin na Nijar sun kama shi ne lokacin da yake yinƙurin satar wasu shanu.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...