Kotu ta bayar da umarnin sakin Sheikh Sani Abdulkadir Zaria

Babbar kotun tarayya dake Abuja ta bayar da umarnin a saki, Sheikh Sani Abdulkadir Zaria ba tare da wani sharadi har ila yau ta kuma  bayar umarnin biyansa diyar naira miliyan 5 saboda yadda aka keta masa haddinsa a matsayinsa na dan adam da hukumomin tsaro su ka yi da kuma wani bankin kasuwanci.

A wani hukunci da kotun ta zartar ranar Litinin, mai shari’a, Peter O. Lifu ya gamsu cewa tsawon lokacin da aka É—auka ana tsare da shehun malamin ba tare da umarnin kotu ba ya keta masa hakkinsa da yake da  shi na mutumtaka a  matsayinsa na mutum, yancinsa da sauraran korafinsa da kuma yancinsa na yin zirga-zirga kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Lauyoyin malamin sun shigar da Æ™arar hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin Æ™asa ta’annati, Hukumar DIA ta  leken asirin ma’aikatar tsaro, ministan shari’a da kuma bankin Jaiz.

Mai Shari’a Lifu ya bawa ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya umarni da ya tabbatar da an aiwatar da hukuncin kotun.

More from this stream

Recomended