Sojoji sun kashe yan bindiga sama da 100 a jihar Kebbi

Dakarun rundunar sojan saman Najeriya na rundunar Operation Hadarin Daji sun kashe yan bindiga sama da 100 a wani jerin hare-hare ta sama da suka kai musu a jihar Kebbi.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi an kai hare-haren ne da yammacin ranar Laraba lokacin da yan bindiga suke tafiya a kauyen Sageko Malekachi na jihar.

Bayanan da aka wallafa sun jiyo wata majiyar sojoji na cewa an kai farmakin ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu cewa yan bindigar na tattaruwa a kauyen Mada dake karamar hukumar Maru ta jihar, Zamfara domin kai hari wasu kauyuka dake jihar Kebbi.

A cewar Zagazola yan bindigar sun yanke shawarar juyawa da baya bayan da suka samu labarin cewa sojojin sama na bibiyarsu.

Daga bisani sojojin suka datse su a kauyen Dan Mani inda suka kashe sama da 100 a dauki ba daÉ—in da aka shafe sama da sa’a guda.

Zagazola ya kara da cewa sojojin kasa sun bi yan bindigar inda suka kashe karin wasu 17 daga cikinsu.

More News

Lauya ya nemi kotu ta bashi mako 4 ya nemo inda Yahaya Bello ya É“uya

Abdulwahab Mohammed babban lauyan tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya nemi babbar kotun tarayya dake Abuja da ta bashi makonni huÉ—u domin ya...

ĆŠalibai 9 aka tabbatar da yin garkuwa da su daga jami’an jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa É—alibai 9 aka tabbatar sun É“ace bayan da wasu Ć´an bindiga suka kai farmaki Jami'ar Kimiya da...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Aƙalla mayaƙan Boko Haram biyu ne suka miƙa kansu ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai a yankin gabashin jihar Borno. Mayaƙan biyu...

Isa Dogonyaro ĆŠan Majalisar Tarayya Daga Jihar Jigawa Ya Rasu

Isa Dogonyaro wakilin al'ummar ƙananan hukumomin Garki da Baɓura a majalisar wakilai ta tarayya ya rasu. Ɗaya daga cikin abokan aikin marigayin a majalisar tarayya,...