Sojoji sun ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su a Kogi

Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta da suka fito daga birged ta 12 sun ceto wasu mutane 6 daga hannun masu garkuwa da mutane a karamar hukumar Yagba East dake jihar Kogi.

A wata sanarwa ranar Talata, Hassan Abdullahi mai magana da yawun birged ta 12 ya ace an ceto mutanen ne  a dazukan Ejiba da Saminaka dake jihar ta Kogi.

Abdullahi ya ce farmaki hadin gwiwa ta sama da ƙasa da taimakon jirgin yan sanda mai saukar ungulu ne ya kai ga kubutar da mutanen bayan da masu garkuwa da su suka tsere suka barsu sakamakon matsin lamba daga  dakarun sojan.

Ya ce farmakin wani ɓangare ne na kokarin da ake wajen shawo kan garkuwa da mutane da ke cigaba da yin ƙamari a fadin jihar.

” Biyar daga cikin mutanen da aka ceto an mika su ga iyalansu a garin Egbe da Ejiba a yayin da mutum na shida ke samun kulawar likitoci,” a cewar sanarwar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]