Bangaren sojan sama na rundunar Operation Hadin Kai ya sanar da kisan Abu Asad ɗaya daga cikin jagororin ƙungiyar Boko Haram.
Ƙarin Æ´an ta’ada da dama aka bada rahoton sun mutu a harin da jiragen yaki suka kai musu a maboyar su dake Tagoshe a tsaunukan Mandara.
Edward Gabkwet daraktan yaÉ—a labarai na Rundunar Sojan Saman Najeriya shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa ranar Asabar a Abuja.
Gabkwet ya ce an kai farmakin ne a ranar Juma’a inda ya ce harin na daga cikin mafi nasara da bangaren sojan sama na rundunar Operation Hadin Kai ya kai a ƴan kwanakin nan.
Ya ce kafin kai harin sojojin saman sun ga Æ´an ta’adda kusan sama da É—ari tare da wasu motocin yaÆ™i huÉ—u suna ta tattaunawa suna raha a tsakanin su a wurin dake da wasu gine-gine uku.
“Biyo bayan kai harin biyu daga cikin ginin sun rushe tare da dukkanin motocin yaÆ™in da aka lalata su”
“Akwai alamu dake nuna cewa Abu Asad wanda Æ™usa ne a Boko Haram bangaren Ali Ngulde da kuma sauran yan ta’ada kamar su Ibrahim Nakeeb, Mujaheed Dimtu, Mustafa Munzir da sauransu na daga cikin Æ´an ta’adda da dama da aka kashe a harin.” a cewar sanarwar.