Peter Obi ya kai  ziyarar jaje kasuwar Singa

Peter ObiTsohon gwamnan jihar Anambra kuma mutumin da ya yiwa jam’iyyar LP takarar shugaban kasa a zaɓen 2023 ya kai ziyarar jaje Kasuwar Dinga dake Kano biyo bayan gobarar da aka yi a wani sashe na kasuwar.

A yayin ziyarar jajen Peter Obi na tare da abokanai  da magoya bayansa ya zagaya kasuwar inda ya jajantawa yan kasuwar kan asarar da suka yi.

Da yake yi yan kasuwar jaje Obi ya bayyana cewa ya zo kasuwar ne domin ya ganewa idonsa irin barnar da gobarar ta yi.

“Wannan babbar asara ce kana iya ganin da kayan  mutane dake ciki wannan babbar asara ce ga masu kayan, ga jihar Kano dama Najeriya baki ɗaya,” a cewar Obi.

Da yake magana a madadin yan kasuwar shugaban kungiyar kasuwar, Alhaji Junaidu Muhammad ya godewa Obi da yan tawagarsa kan ziyarar da su ka kawo.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]