Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya a zaɓen 2023, Peter Obi, ya tabbatar da ficewarsa daga jam’iyyar ADC mai haɗaka.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Lahadi, Obi ya bayyana cewa ya ɗauki wannan mataki ne sakamakon rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar.
Ya ce irin rikicin da ya yi ƙoƙarin kaucewa a tsohuwar jam’iyyarsa ta LP ne ya sake bayyana a ADC. Sai dai ya jaddada cewa bai fice ba ne saboda wani jigo ya ɓata masa rai, yana mai cewa, “Ban ɗauki matakin saboda shugaban jam’iyyar, David Mark ko Atiku ko wani jigo a jam’iyyar ya yi min wani abu ba”.
A halin yanzu, jam’iyyar ADC na fama da rikicin shugabanci da ke gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda wani ɓangare ke ƙalubalantar sahihancin shugabannin jam’iyyar.
Haka kuma, akwai rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigai ciki har da Obi da Rabiu Musa Kwankwaso na iya sauya sheka zuwa wata jam’iyya, kodayake har yanzu ba a tabbatar da hakan ba.
Peter Obi Ya Fice Daga Jam’iyyar ADC Saboda Rikici

