Tsohon Gwamnan Jihar Delta kuma dan takarar mataimakin shugaban kasa a inuwar jam’iyyar PDP a zaben 2023, Ifeanyi Okowa, ya bayyana cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP kafin zaben 2027.
Okowa, wanda kwanan nan ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise News a ranar Talata.
A cewarsa: “Na shaida masa cewa muna da taron shugabanni da za mu gudanar a makon da ya gabata, kuma sakamakon wannan taro ne zai fitar da matsayar da za mu dauka. Mun kasa jin dadin halin da PDP ke ciki. Har ila yau, daga cikin sakonnin da ya aiko min, na fahimci cewa shima Atiku yana shirin barin PDP – kuma al’umma sun riga sun fara ji da hakan.”
Rahotanni sun nuna cewa a ranar 20 ga Maris, 2023, Atiku Abubakar tare da Peter Obi na jam’iyyar Labour Party, da tsohon Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai, da wasu shugabannin siyasa sun kafa wani kawance da nufin kalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben shekarar 2027.
Wannan cigaba ya haifar da muhawara mai karfi a tsakanin ’yan siyasa da jama’a, musamman game da yiyuwar hada kai tsakanin manyan ’yan adawa domin fuskantar APC a zaben mai zuwa.
Okowa Ya Ce Atiku Yana Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar PDP
