Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa zai tattauna ta waya da shugaban Amurka Donald Trump a yau kan wasu muhimman batutuwa da suka shafi yankin Gabas ta Tsakiya.
Netanyahu ya bayyana hakan ne yayin wani taro na musamman da jami’an gwamnati suka gudanar domin bikin ranar Jerusalam.
A cewarsa, “Idanunmu na kan Iran. Zan yi magana da abokinmu shugaba Trump a yau, kamar yadda nake yi a ƴan kwanakin nan.”
Ya kuma ce yana sa ran jin bayanin ci gaban da aka samu bayan ziyarar da Trump ya kai China da kuma wasu batutuwa na daban.
“Akwai abubuwa da dama da za su iya faruwa, kuma a shirye muke kan kowane yanayi,” in ji Netanyahu.
Netanyahu Zai Tattauna Da Trump Kan Iran Da Sauran Batutuwa

