Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran kayayyakin more rayuwa.
Sakataren zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA), Hannafi Fagam, ya ce gwamnatin jihar ta ware kudade domin kai dauki ga wadanda abin ya shafa, yayin da ake ci gaba da tantance irin barnar da aka yi. Haka kuma ya yi kira ga kungiyoyin agaji, abokan hulda na kasa da kasa da masu hannu da shuni da su ba da gudummawa domin tallafa wa mutanen da guguwar ta shafa.
Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

