Matasa sun ƙona ofishin INEC a Benue

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa INEC ta ce an ƙona ofishin hukumar dake yankin Sankara a ƙaramar hukumar Ukum ta jihar Benue.

A wata sanarwa ranar Laraba, Sam Olumekun kwamishinan hukumar na sadarwa da kuma wayar da kan masu kaɗa riƙa ya ce Sam Egwu  kwamishinan zaɓe na jihar ne ya bayyana haka.

Ya ce matasan  yankin dake gudanar da zanga-zanga kan matsalar ƴan fashin daji a yankin su ne su farma ofishin hukumar da kuma wasu ofisoshin gwamnati da ƙarfe biyu na rana.

Sanarwar ta ƙara de cewa duk da cewa ba a samu asarar rayuka ba amma an samu asarar kayayyaki ofisoshi da kuma na aikin zaɓe.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]