Gwamna Alia Ya Bukaci APC Ta Mara Wa Tinubu Baya a 2027

Gwamnan jihar Benuwe, Hyacinth Alia, ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar APC da su fito da yawa domin zaɓar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2027.

Alia ya bayyana hakan ne bayan tantance shi a zaɓen fidda gwani na gwamna da aka gudanar a mazabarsa ranar Alhamis.

Ya ce Tinubu ya cancanci sake komawa mulki domin ci gaba da ayyukan raya ƙasa, gyaran tattalin arziƙi, samar da ayyukan yi da kuma inganta tsaro.

Gwamnan ya kuma yi alƙawarin sasanta ‘ya’yan jam’iyyar APC da suka rasa tikitin takara domin su ci gaba da haɗa kai wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar a zaɓe masu zuwa.

Alia ya bayyana gamsuwarsa da yadda magoya bayan APC suka fito domin zaɓen fidda gwani, yana mai cewa hakan alama ce ta goyon bayan al’umma gare shi da jam’iyyar APC.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]