An Yi Jana’izar Mutum 16 Da Aka Kashe A Benue



An gudanar da jana’izar mutum 16 da ake zargin wasu ’yan bindiga ne suka kashe a ƙauyen Efeyi, da ke jihar Benue, a ranar 8 ga Agusta.

Rahotanni sun ce mutanen sun rasa rayukansu ne yayin wani hari da aka kai ƙauyen a ranar 28 ga Yuli, wanda ya haifar da fargaba tare da tilasta wa wasu mazauna yankin tserewa.

’Yan uwa, shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, ’yan siyasa da malaman addini sun halarci jana’izar domin yin bankwana da waɗanda aka kashe.

An gudanar da addu’o’in jana’izar ne ƙarƙashin jagorancin wani limamin Cocin Katolika, kafin a binne gawarwakin yayin da ’yan uwa da makusanta ke zaman makoki.

Harin ya zo ne bayan wasu hare-hare da suka yi sanadin mutuwar mutane a wasu ƙauyukan gundumar Ugboju, cikin ƙaramar hukumar Otukpo.

More from this stream

Recomended