Kwankwaso ya Kaddamar da sabuwar Kungiyar siyasa

Tsohon gwamnan jihar Kano da ke arewacin Najeriya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, yana jagorantar wani gagarumin taro na wasu manyan siyasar kasar karkashin wata kungiya mai suna The National Movement TNM.

Fitattun mutane da Æ´an siyasa da suka halarci taron sun haÉ—a da Alhaji Tanko Yakasai da Capt Idris Wada, tsohon gwamnan Kogi da Rufai Alkali da Aminu Ibrahim Ringim, tsohon dan takarar gwamna a jihar Jigawa da kuma Inijiniya Buba Galadima.

Ana gudanar da taro ne a International Conference Centre da ke Abuja, babban birnin tarayyar kasar.

A jawabin Kwankwaso, ya ce wasu ƴan Najeriya ne da suka damu da abin da ke faruwar a ƙasar suka haɗa kai don ceto ta daga mawuyacin halin da ta shiga.

Ya ce yunƙuri ne na ƴan Najeriya masu kishi da suke zaune a gida da kasashen waje.

A cewar Kwankwaso za su duƙufa wajen farfaɗo da tattalin arzikin kasar da inganta rayuwar ƴan kasa a birni da karkara

Ya ce sun shirya tsaf domin tunkarar matsalar tsaro da ta addabi Najeriya.

Kwankwaso ya ce za su yi wa makiyaya gata na ganin cewa ba a cinye musu burtalai ba, sannan za su bai wa manoma dukkan kariyar da suke bukata.

Tsohon gwamnan na jihar Kano, wanda dan jam’iyyar PDP ne, bai bayyana mukamin da yake son nema ba a wannan sabuwar kungiya ta siyasa.

Sai dai ana rade radin cewa zai fita daga jam’iyyar PDP sakamakon rashin jin dadin abubuwan da ke faruwa a cikinta. Kodayake bai tabbatar da hakan ba.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...