Kotun ɗaukaka ƙara ta mayar wa gwamnan Nasarawa kujerarsa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja a ranar Alhamis ta tabbatar da nasarar gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, saɓanin hukuncin da kotun sauraron ƙararrakin zabe ta zarta.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta bayyana Sule na jam’iyyar All Progressives Congress a matsayin wanda ya lashe zaben, yayin da David Ombugad na jam’iyyar Peoples Democratic Party ya zo na biyu.

Sai dai kotun da mai shari’a Ezekiel Ajayi ya jagoranta a wata shari’ar raba gardama ta yanke cewa bisa ga hujjojin da aka samu daga rumfunan zabe daban-daban da ke gaban kotun, Ombugadu ya samu rinjayen kuri’u a zaben.

Amma Sule ya daukaka kara kan hukuncin inda ya bukaci kotun daukaka kara da ta ajiye shi a gefe.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...