Tinubu ya bada tallafin naira biliyan 2 ga wanda rikicin Jos ya shafa

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince a fitar da kudi naira biliyan 2 domin tallafawa mutanen da harin ranar 29 ga watan Maris ya shafa a Anguwar Rukuba dake jihar Filato.

Akalla mutane 28 ne suka mutu bayan da wasu yan bindiga suka bude wuta a wata mashaya dake unguwar.

Bayo Onanuga mai magana da yawun shugaban kasar ne ya bayyana haka a ranar Laraba a cikin wata sanarwa da ya fitar  inda ya ce ministan jinkai da yaÆ™i da talauci, Mohammed Doro ne ya bayyana haka a wurin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Abuja.

Onanuga ya ce taron da ya samu halartar masu ruwa da tsaki su 32 daga jihar Filato an gudanar da shi ne domin lalubo hanyar da za ta kawo karshen kashe-kashe dake yawan faruwa a jihar.

Da yake magana a madadin tawagar gwamnan jihar, Caleb Mutfwang ya yi marhabin da tallafin na gwamnatin tarayya ya kara da cewa wannan ne karon farko da dukkanin tsofaffin gwamnonin jihar su ka haÉ—u wuri guda domin tattauna batun zaman lafiya.

Ya kuma tabbatarwa da shugaban ƙasa cewa masu ruwa da tsakin za su yi aikin wajen aiwatar da matakan da aka cimma a wurin taron.

More from this stream

Recomended