Aƙalla mutum 22 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu kusan 40 suka samu raunuka sakamakon taho-mu-gama tsakanin motocin bas biyu a kusa da Madawa, kudancin Nijar.
Ma’aikatar Sufuri ta Nijar ta bayyana cewa mutum 17 daga cikin waɗanda suka mutu sojoji ne da ke cikin ɗaya daga cikin motocin.
Mahukunta sun ce har yanzu ba a gano musabbabin hatsarin ba, yayin da ake gudanar da bincike domin gano abin da ya jawo lamarin.
Hatsarin ya faru ne a lokacin da hukumomin ƙasar ke gudanar da wani shiri na wayar da kan jama’a kan bin dokokin kiyaye haɗurran hanya.
A Nijar, haɗurran ababen hawa na yawan faruwa, inda sama da mutum 1,200 suka mutu sakamakon hatsarin hanya a shekarar 2025.
Mutum 22 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Nijar

