Houthi Sun Kai Hari Kan Matatar Man Saudiyya



Mayakan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan matatar man fetur ta Aramco da ke Jazan, a gabar Bahar Maliya.

Kakakin rundunar ƙungiyar, Yahya Saree, ya ce harin ya kasance martani ne ga abin da ya kira kutsen Saudiyya a arewa maso yammacin Yemen.

Sai dai Ma’aikatar Makamashi ta Saudiyya ta bayyana cewa jami’an kashe gobara sun yi nasarar shawo kan gobarar da ta tashi a wurin.

Harin ya zo ne a yayin da rikici tsakanin Houthi da Saudiyya ke ƙara tsananta, lamarin da ke ƙara jefa matsin lamba kan samar da makamashi a duniya.

A wani ci gaba, Iran ta yi gargadin cewa ba za ta buɗe mashigar ruwan Hormuz ba har sai Amurka ta amince da wasu buƙatunta, ciki har da sassauta takunkuman da aka kakaba mata da kuma biyan diyya kan barnar da yaƙi ya haddasa.

More from this stream

Recomended