Kotun Ƙolin Amurka ta yi watsi da wani umarni da shugaban ƙasar Donald Trump ya nemi aiwatarwa domin kawo ƙarshen bai wa jariran da aka haifa a Amurka damar zama ’yan ƙasa kai tsaye.
Alƙalan kotun shida sun goyi bayan hukuncin, inda suka tabbatar da cewa haƙƙin samun ɗan ƙasa ta hanyar haihuwa yana kunshe cikin kundin tsarin mulkin ƙasar. Sai dai wasu alƙalai uku sun nuna rashin amincewa da hukuncin.
Donald Trump ya bayyana matakin kotun a matsayin “abin takaici,” amma ya ce “Majalisar Dokoki za ta iya kafa doka akan hakan.”
Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama sun yi maraba da hukuncin, suna masu cewa ya kare wani muhimmin hakki da kundin tsarin mulkin Amurka ya tanada.
A watan Afrilu ne Trump ya zama shugaban Amurka na farko da ke kan mulki da ya halarci zaman Kotun Ƙoli yayin sauraron shari’a, duk da cewa ya bar kotun kafin a kammala zaman.
Kotun Ƙolin Amurka Ta Yi Watsi Da Yunkurin Trump Na Dakatar Da Haihuwar ’Yan Ƙasa

