A ranar Alhamis Kotun Ƙoli za ta yanke hukuncin karar rikicin shugabancin jam’iyar ADC

Kotun Ƙolin Najeriya ta saka ranar Alhamis  30 ga watan Afrilu a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan rikicin shugabancin jam’iyar ADC.

Tun da farko kotun ƙolin ta jingine batun ranar yanke hukuncin tun bayan da ta saurari lauyoyin ɓangarorin biyu na masu ƙara da kuma wanda ake ƙara abun da ya jawo jagorancin jam’iyyar ADC ya rubutawa alkalin alkalai na kasa wasika dake neman a gaggauta yanke hukuncin saboda yadda wa’adi ke nema ya kure.

Amma kuma a ranar Laraba kotun ƙolin ta sanar da cewa da misalin karfe 02:00 na ranar Alhamis ne za ta yanke hukunci

Alkalan kotun ƙolin su biyar ƙarƙashin jagorancin mai sharia, Muhammad Garba ne za su yanke hukuncin.

Shugabancin jam’iyar ADC ƙarƙashin jagorancin David Mark ne suka shigar da ƙara gaban kotun inda suke ƙalubalantar hukuncin ranar 12 na kotun daukaka kara da ya jawo hukumar zaɓe ta ƙasa ta cire sunansu daga jerin shugabannin jam’iyar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]