Jami’an tsaro sun gano AK-47 sama da 150 a wani gida Minna

An samu yamutsi a Minna babban birnin jihar Niger, lokacin da wani da ake zargin É—an kungiyar Boko Haram ne ya yi musayar wuta da jami’an tsaro da tsakar daren ranar Talata.

Jami’an tsaro sun kaddamar da farmaki a yankin Gegbanu dake Minna inda gidan wanda ake zargin yake.

A cewar jaridar Dailly Trust an gano bindigogi kirar AK-47 da basu gaza guda 150 ba, harsashi 3000, bama bamai, rokoki da kuma bindigar kakkaɓo jiragen sama duka a gidan.

Wani maigadi dake aiki a gidan dake makotaka da gidan da aka kai farmakin ya samu raunin harbin bindiga inda yake samun kulawar likitoci a asibitin kwararru na IBB dake Minna.

Mazauna unguwar sun ce da karfe 12:00 aka kai farmaki kuma an É—auki tsawon sa’o’i ana musayar wuta da mutumin kafin daga bisani ya tsere.

Rahotanni sun bayyana cewa yayi mutumin yayi amfani da bindigar roka inda ya rusa wani sashe na katangar gidan ya kuma tsere sai dai jami’an tsaro sun samu nasarar kama Æ´aÆ´ansa da matarsa.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...