An samu yamutsi a Minna babban birnin jihar Niger, lokacin da wani da ake zargin É—an kungiyar Boko Haram ne ya yi musayar wuta da jami’an tsaro da tsakar daren ranar Talata.
Jami’an tsaro sun kaddamar da farmaki a yankin Gegbanu dake Minna inda gidan wanda ake zargin yake.
A cewar jaridar Dailly Trust an gano bindigogi kirar AK-47 da basu gaza guda 150 ba, harsashi 3000, bama bamai, rokoki da kuma bindigar kakkaɓo jiragen sama duka a gidan.
Wani maigadi dake aiki a gidan dake makotaka da gidan da aka kai farmakin ya samu raunin harbin bindiga inda yake samun kulawar likitoci a asibitin kwararru na IBB dake Minna.
Mazauna unguwar sun ce da karfe 12:00 aka kai farmaki kuma an É—auki tsawon sa’o’i ana musayar wuta da mutumin kafin daga bisani ya tsere.
Rahotanni sun bayyana cewa yayi mutumin yayi amfani da bindigar roka inda ya rusa wani sashe na katangar gidan ya kuma tsere sai dai jami’an tsaro sun samu nasarar kama Æ´aÆ´ansa da matarsa.