Haɗarin tankar mai ya yi ajalin mutane kusan 30 a Neja

Fashewar wata tankar mai ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 30 a hanyar Agaie-Bida a jihar Neja da safiyar Lahadi

Rahotanni sun tattaro cewa tankar ta yi karo ne da wata tirela da ke dauke da shanu kuma ta nufi jihar Legas daga Wudil, jihar Kano.

Babban daraktan hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Neja, Mallam Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Zuwa yanzu dai ba a samu rahoton abin da hukumar kiyaye haɗɗura a Najeriya (FRSC) ta ce kan hadarin ba.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]