Gbajabiamila zai yi murabus daga majalisar wakilai a yau

A yau ne ake sa ran Femi Gbajabiamila, tsohon kakakin majalisar wakilai zai yi murabus daga majalisar wakilai.

Domin karbar ragamar shugabancin ma’aikatan fadar shugaban kasa karkashin Bola Tinubu.

Ku tuna cewa an nada Gbajabiamila a matsayin babban hafsan ma’aikatan shugaba Tinubu a ranar 2 ga watan Yuni.

Bugu da kari, shugaban ya nada Sen. Ibrahim Hadejia, tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa a matsayin mataimakin shugaban ma’aikata da George Akume, tsohon ministan ayyuka na musamman a matsayin sakataren gwamnatin tarayya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]