Modi Ya Gayyaci Tinubu Taron BRICS

Muhammadu SabiuHausa51 minutes ago



Firaministan Indiya, Narendra Modi, ya gayyaci Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, zuwa taron ƙungiyar ƙasashen BRICS da za a gudanar a bana.

Gayyatar na zuwa ne a wani mataki na ƙarfafa dangantaka da haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Indiya a fannoni daban-daban.

Najeriya ta samu matsayin ƙasa abokiyar hulɗa da BRICS a shekarar 2025. Sai dai har yanzu ba ta samu cikakken matsayin mamba ba, ko da yake tana halartar wasu tarurruka da shirye-shiryen ƙungiyar.

Masana sun bayyana gayyatar a matsayin wata dama da Najeriya za ta iya amfani da ita wajen bunƙasa cinikayya, zuba jari, haɗin gwiwar fasaha da sauran harkokin tattalin arziki tare da Indiya da sauran ƙasashe masu tasowa.

Babban jami’in diflomasiyyar Indiya a Najeriya, Abhishek Singh, ya ce haɗin gwiwar ƙasashen biyu bai tsaya kan kasuwanci kadai ba, domin ya shafi makamashi, tsaro, lafiya, noma, fasaha da tsaron teku.

Ana sa ran halartar taron za ta ƙara ƙarfafa dangantakar Najeriya da ƙasashen BRICS, tare da samar da ƙarin damammaki ga tattalin arzikin ƙasar.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...