Dattawan Kiristoci Sun Bukaci A Tura Jami’an Tsaron Dazuka Zuwa Sambisa


Dattawan Kiristoci daga jihohin Borno da Adamawa sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta tura jami’an tsaron dazuka zuwa dajin Sambisa domin ƙara ƙaimi wajen yaƙi da masu tayar da ƙayar baya a Arewa maso Gabas.

Sun bayyana hakan ne a Abuja bayan kammala wani shirin azumi da addu’a na kwanaki uku da shugabannin al’ummar Marghi suka shirya.

Dattawan sun bukaci gwamnati ta ƙara yawan jami’an tsaro a yankunan da ke kewaye da dajin Sambisa, musamman a ƙananan hukumomin Madagali, Askira/Uba, Chibok da Gwoza.

Sun kuma nuna damuwa kan hare-haren da ake kai wa al’umma da kuma sace yara a wasu yankunan Borno da Oyo, suna masu cewa matsalar tsaro ta fi yadda mutane da dama ke zato muni.

Baya ga haka, sun yi kira da a inganta tattara bayanan sirri tare da amfani da fasahar zamani domin taimakawa wajen ceto waɗanda aka sace da kuma dakile ayyukan masu tayar da ƙayar baya a yankin.

More from this stream

Recomended