Dakarun Najeriya sun hallaka ƴanbindiga a Neja

Rundunar sojin saman Najeriya ta hakala ‘yanbindiga sama da 28 a yankin ƙaramar hukumar Shiroro dake jihar Neja.

Wata sanarwa da mataimakin daraktan yaɗa labarai na rundunar, Guruf Kaftin Kabiru Ali, ya fitar ranar Alhamis ta ce an kashe ‘yanbindigar ne a wani hari ta sama da jami’an rundunar suka kai musu ranar Laraba 11 ga watan Satumba, kamar yadda jaridun ƙasar suka ruwaito.

Kafofin yada labaru sun ambato sanarwar na cewa, “An kai harin ne kan ‘yanbindigar a yankin Bassa, bayan da jami’anmu suka samu kiran gaggawa daga sauran jami’an tsaro a yankin.

“A lokacin da sojojin saman suka isa yankin, jirginsu ya hangi ‘yan bindigar su fiye da 100 suna musayar wuta da jami’an tsaron da ke ƙasa, bayan jami’anmu sun fahimci inda sojoji suka tsaya, sai jirginmu ya buɗe wa ‘yanbindigar wuta bayan ya gono inda su ma suka tsaya.

“Harin jirgin ya yi nasara, inda ya kashe gomman ‘yanbindigar, kuma kawo yanzu mun gano gawarwaki 28 a yankin, inda kuma wasu da dama suka ƙone tare da babura da makamansu.”

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]