Atiku ya karɓi ɓakuncin wasu manyan ƴan siyasa

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya karbi bakuncin iyalan mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai a gidansa dake unguwar Asokoro a Abuja.

Makasudin ziyarar ta su shi ne neman auren ƴarsa, A’isha Atiku  Abubakar.

A cikin manyan baƙin da suke cikin tawagar akwai mai bawa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido da na jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]