An kashe gawurtaccen É—an bindiga Janari a wani harin sojan saman Najeriya a Kaduna

An kashe riƙaƙƙen dan fashin daji kuma mai garkuwa da mutane a tare da wasu muƙarrabansa a wani hari da sojan saman Najeriya suka kai ranar Asabar.

Mai magana da yawun rundunar sojan saman Najeriya, AVM Edward Gabkwet shi ne ya bayyana haka a Abuja ranar Lahadi inda ya ce Janari da abokan ta’asarsa su ne ke da alhakin kai hare-hare da yin garkuwa da mutane a jihar Kaduna da kuma kan titin Kaduna zuwa Abuja.

Ya ce harin sama da bangaren sojan sama na rundunar ” Operation Whirl Punch” ya kai an amince tare da aiwatar da shi bayan da aka gano Janari da muÆ™arrabansa a wani wuri dake kusa da Gadar Katako a Æ™aramar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

Gabkwet ya ce shawagin tattara bayanai da jirgin ya yi ya gano cewa gungun Æ´an bindigar suna tattaruwa domin kai hari ko kuma garkuwa da mutane abin yasa aka kai harin kenan.

Mai magana da yawun rundunar ya kara da cewa an kai hari makamancin haka a wata maɓoyar yan fashin daji dake Chukwuba a jihar Niger.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...