An kama masu safarar yara ƙanana a Jihar Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane 9 da ake zargi da tsunduma a harkar safara da sace-sace da siyar da kananan yara a tsakanin jihohi.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Usaini Gumel ne ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar rundunar ta Bompai a ranar Alhamis.

Ya bayyana cewa, an kama wadanda ake zargin ne bayan gudanar da wasu ayyuka da hukumar leken asiri ta gudanar, inda aka gano tsawon lokaci da aka kwashe ana gudanar da safarar yara a sassan jihohin Kano, Bauchi, Gombe, Legas, Delta, Anambra da Imo.

A cewar Gumel, an ceto jimillar mutane bakwai wadanda akasarinsu yara kanana ne.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]