Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane 9 da ake zargi da tsunduma a harkar safara da sace-sace da siyar da kananan yara a tsakanin jihohi.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Usaini Gumel ne ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar rundunar ta Bompai a ranar Alhamis.
Ya bayyana cewa, an kama wadanda ake zargin ne bayan gudanar da wasu ayyuka da hukumar leken asiri ta gudanar, inda aka gano tsawon lokaci da aka kwashe ana gudanar da safarar yara a sassan jihohin Kano, Bauchi, Gombe, Legas, Delta, Anambra da Imo.
A cewar Gumel, an ceto jimillar mutane bakwai wadanda akasarinsu yara kanana ne.