Uba da yarsa sun faɗa rijiya sun mutu a Kano

Wani uba da kuma matashiyar yarsa sun rasa rayukansu bayan da suka fada wata tsohuwar rijiya a kauyen Yancibi dake karamar hukumar Tsanyawa ta jihar Kano.

Lamarin da ya faru a ranar Talata ya rutsa da Abubakar Abdullahi mai shekaru  45 da kuma yarsa Fiddausi  mai shekaru 15.

A cewar mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta tarayya, Saminu Yusuf Abdullahi, Fiddausi ta faɗa rajiyar ne bisa tsautsayi.

Mahaifin nata ya shiga cikin rajiyar ne a ƙoƙarin da niyyar ya ceto ta.

Ya ce ma’aikatan aikin ceto daga ofishin hukumar dake Tsanyawa sun yi gaggawar isa wurin amma suka gaza kammala aikin ceton saboda duhu da kuma rashin kyawun yanayi.

Ya kara da cewa daga baya an tura wata tawaga daga hedkwatar hukumar domin taimakawa wajen aikin ceto kuma sun samu nasarar fito da mutane biyun ba a cikin hayyacinsu amma daga baya likitoci sun tattabatar da mutuwarsu.

Daga bisani an mika gawarwakin hannun Dagacin Yancibi, Shamsu Sani.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]