Gwamnatin Jihar Anambra ta tabbatar da kama Fasto Harrison Charles, mamallakin cocin Day Spring Assembly da ke Awada a birnin Onitsha, bisa wasu zarge-zarge masu nasaba da karɓe matan aure daga mazajensu.
Mai bai wa gwamnan jihar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Dakta Ejimofor Opara, ya bayyana cewa jami’an tsaro ne suka kama faston bayan wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta ya ƙunshi zarge-zarge a kansa.
A cewarsa, an miƙa Fasto Harrison ga rundunar ’yan sanda, kuma an fara gudanar da bincike haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da rundunar ’yan sandan Anambra.
Rahotanni sun ce wasu mambobin cocin sun zarge shi da tilasta musayar mata da kuma auren matan wasu mambobi.
Opara ya kuma bayyana cewa an gano jarirai goma sha ɗaya a gidan faston lokacin da aka kama shi. Ya ce faston ya yi ikirarin cewa shi ne mahaifin dukkan jariran kuma sun fito ne daga matansa goma sha ɗaya.
Ya ƙara da cewa bincike na ci gaba, yayin da gwamnati ta buƙaci duk wanda ke da ƙarin bayani kan lamarin ya tuntubi hukumomin jihar.
An Kama Fasto Da Ake Zargi Da Mallake Matan Aure Da Nufin Mayar Da Su Matansa

