Yara Uku Sun Mutu A Gidan Mai Maganin Gargajiya A Anambra



Yara uku sun mutu, yayin da wani yaro guda ke kwance cikin mawuyacin hali a asibiti bayan an tsince su a gidan wata mai maganin gargajiya a ƙauyen Umuoduba, Ƙaramar Hukumar Idemili North ta Jihar Anambra.

Lamarin ya faru ne a tsakar daren Laraba, inda mazauna garin suka tsinci yaran huɗu a sume a cikin gidan.

An tabbatar da mutuwar yara uku, yayin da aka garzaya da na huɗu zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci.

Rahotanni sun ce shekarun yaran sun kai tsakanin 6 zuwa 15, sai dai ba a tabbatar da asalinsu ko yadda suka tsinci kansu a gidan ba.

Jami’an ’yan sanda daga Ogidi, tare da wasu shugabannin al’umma, sun fara ɗaukar matakan bincike kan lamarin.

A halin yanzu, hukumomi na ƙoƙarin gano ainihin abin da ya jawo mutuwar yaran.

More from this stream

Recomended