An gano gawar wata mata, ɗanta mai shekara huɗu da kuma wani mutum da aka fi sani da Shanko a gidansu da ke yankin Egbe Subair a garin Ijebu-Igbo na Jihar Ogun.
Rahotanni sun nuna cewa an samu gawar matar da mutumin a bayan gidan da suke zaune, yayin da aka samu gawar yaron a ɗaya daga cikin dakunan gidan.
Wasu mazauna yankin da suka kai ziyara wurin sun bayyana cewa an ga wasu kayayyaki da sassan bayan gidan sun lalace, lamarin da ya sa ake zargin cewa an yi wata fafatawa kafin mutuwar mutanen.
Sai dai wasu daga cikin al’ummar yankin na hasashen cewa yiwuwar guba ce ta haddasa mutuwar tasu.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Ogun, DSP Oluseyi Babaseyi, ya ce rundunar tana bincike domin gano hakikanin abin da ya faru.
Ya kuma bayyana cewa an kai gawarwakin zuwa ɗakin ajiye gawa na Babban Asibitin Ijebu-Igbo domin ci gaba da bincike.
An Gano Gawar Wata Mata Da Ɗanta Da Kuma Wani Mutum Guda A Cikin Gida

