An kai sabon hari a Jihar Zamfara

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a unguwar Nasarawa da ke garin Maru, hedikwatar ƙaramar hukumar Maru a jihar Zamfara.

Da sanyin safiyar Juma’a ne maharan suka mamaye yankin inda suka yi ta harbe-harbe don tsorata mazauna yankin.

An ce sun isa ƙaramar hukumar ne da yawansu ɗauke da makamai.

Hukumomin ‘yan sanda a jihar har yanzu ba su tabbatar da sabon harin ba.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Zamfara Yazid Abubakar bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.

Sai dai wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilai na tsaro ya shaida wa wani gidan talabijin cewa Dakarun Operation Hadarin Daji sun yi gaggawar amsa kiran da suka yi musu.

An yi musayar wuta da aka kwashe sama da awanni biyu ana yi.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...