
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya yabawa dakarun sojan Najeriya na rundunar haɗin gwiwa ta Operation Fansan Yamma kan nasarar da su ka samu a yaƙin da su ke da yan ta’adda a jihar.
A wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi, Sulaiman Idris mai magana da yawun gwamnan ya ce dakarun sun ƙaddamar da wani tsararren farmaki lokaci guda da tsakar daren ranar 7 ga watan Mayu a ƙananan hukumomin Kaura Namoda da Birnin Magaji dake jihar.
Farmakin dakarun ya kai ga kisan wasu jagororin yan bindiga tare da gano tarin makamai ciki har da bindiga AK-47, Machine Gun, bindiga ƙirar gida da kuma harsashi guda 571 da ɗaya.
Lawal ya ce an kai farmakin a lokacin da ya dace bayan makamancin sa da aka kai ranar 10 ga watan Mayu da ya tarwatsa taron shugabannin yan bindiga a ƙauyen Tumfa dake karamar hukumar Shinkafi.
Gwamnan ya ce bayanan sirri sun nuna cewa yan bindigar sun tattaru a wata maɓoya domin su tsara yadda za su kai farmaki garuruwa dake jihar.
Ya ƙara da cewa sashen sojan sama na rundunar Operation Fansan Yamma ya kai masu farmaki inda ya lalata matattarar ta su.

