A Fara Duba Watan Shawwal Gobe Alhamis — Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Sa’ad Abubakar, ya fitar da sanarwar umurtar Musulmi da su nemi jinjirin watan Shawwal 1444H daga yau Alhamis.

Sarkin ya yi fitar da wannan sanarwar ne a cikin wata takarda dauke da sa hannun shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addini a Majalisar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo Junaidu a ranar Laraba.

A dokar addinin Musulunci dai, ganin jinjirin watan Shawwal shi ke alamta kawo ƙarshen watan Ramadan wanda Musulmi suke shafe dukkaninsa suna azumi a ciki.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]