A Fara Duba Watan Shawwal Gobe Alhamis — Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Sa’ad Abubakar, ya fitar da sanarwar umurtar Musulmi da su nemi jinjirin watan Shawwal 1444H daga yau Alhamis.

Sarkin ya yi fitar da wannan sanarwar ne a cikin wata takarda dauke da sa hannun shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addini a Majalisar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo Junaidu a ranar Laraba.

A dokar addinin Musulunci dai, ganin jinjirin watan Shawwal shi ke alamta kawo ƙarshen watan Ramadan wanda Musulmi suke shafe dukkaninsa suna azumi a ciki.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]