Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya maka Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) a kotu, kamar yadda mai magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye, ya bayyana a shafinsa na X.
An ce El-Rufai ya shigar da ƙara a babbar kotun tarayya da ke Abuja. Ya roƙi kotun ta ayyana takardar izinin shiga binciken gidansa a matsayin mara inganci. Haka kuma ya nemi kotun ta tabbatar da cewa an tauye masa haƙƙinsa.
Bugu da ƙari, ya buƙaci kotun ta umarci ICPC ta mayar masa da kayayyakin da aka kwaso daga gidansa. Ya kuma roƙi a hana hukumar amfani da kayayyakin a nan gaba.
Rahotanni sun nuna cewa El-Rufai na tsare a hannun ICPC. Haka kuma jami’an hukumar sun kai bincike gidansa domin ci gaba da gudanar da bincike kan zarge-zargen da ake masa.
Tun da farko, Hukumar EFCC ce ta fara tsare shi. Daga bisani aka ce an miƙa shi ga ICPC, wadda ita ma ke gudanar da nata bincike daban.
El-Rufai Ya Maka ICPC A Kotu Kan Binciken Gidansa

