Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta tabbatar da kama Farfesa Bello Abubakar, likitan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, bisa zargin bayar da bayanan karya bayan ziyarar da El-Rufai ya kai asibiti da izinin kotu.
ICPC ta ce an kai El-Rufai bangaren masu zaman kansu na Asibitin Kasa da ke Abuja domin duba lafiyarsa, amma ziyarar ta sabawa abin da kotu ta amince da shi.
Hukumar ta ce wani sakon da dan takarar gwamna na jam’iyyar ADC a Kaduna, Isa Ashiru Kudan, ya wallafa tare da hotuna ya nuna cewa an gudanar da wata ganawa da El-Rufai yayin da ya kamata yana duba lafiya.
A cewar ICPC, hakan ya saba wa umarnin kotu, saboda haka aka kama Farfesa Bello Abubakar bisa zargin bayar da bayanan karya, yayin da bincike ke ci gaba.
Lamarin ya biyo bayan kin amincewar babbar kotun Kaduna da bukatar El-Rufai ta neman beli a karo na uku a shari’ar da ICPC ke yi da shi.
ICPC Ta Yi Bayanin Dalilin Kama Likitan El-Rufai

