Mutuwar Attahiru Za Ta Mayar Da Hannun Agogo Baya

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya kwatanta rasuwar babban hafsan sojojin kasa Laftanar Janar Ibrahim Attahiru a matsayin wani abu da zai haifar da koma baya ga kasar.

Buhari ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakinsa Garba Shehu ya fitar a ranar Juma’a sa’o’i bayan rasuwarsa.

Janar Attahiru ya rasu ne a wani hadarin jirgi da ya auku a kusa da filin tashin jirage da ke Kaduna a arewa maso yammacin kasar.

“Hadarin jirgin, ya yi mana kwaf daya a makasa, a kuma daidai lokacin da dakarunmu suka samo bakin zaren kawo karshen matsalar rashin tsaro da kasar ke fuskanta.” Buhari ya ce a sanarwa ta Shehu wacce ya wallafa a shafin Twitter.

Buhari wanda ya yi addu’a ga mamatan, ya sha alwashin ba za a manta da irin saudakarwar da suka yi ba.

A watan Janairu, Buhari ya nada Janar Attahiru, wanda ya gaji Janar Tukur Buratai tare da sauran hafsoshin sojojin kasar.

Wannan shi ne karo na uku a wannan shekara da jirgin sojin Najeriya ke yin hatsari ko ya bata a neme shi a rasa.

Lokacin da ministan tsaron Najeriya yake yi wa Shugaba Buhari kan hadarin jirgin (Twitter/@BashirAhmaad)
Lokacin da ministan tsaron Najeriya yake yi wa Shugaba Buhari kan hadarin jirgin (Twitter/@BashirAhmaad)

A halin da ake ciki fadar shugaban kasar, ta fitar da sunayen mutum 11 da suka mutu a hatsarin jirgin:

– Lt Gen. I. Attahiru

– Brig Gen. MI Abdulkadir

– Brig Gen. Olayinka

– Maj. LA Hayat

– Maj. Hamza

– SGT Umar

Matuka Jirgin Da Masu Hidima

– FLT LT TO Asaniyi

– FLT LT AA Olufade

– ACM Oyedepo

More from this stream

Recomended