Ƴan sanda sun kama yaron da ya cire wa manomi hannu

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wani makiyayi dan shekara 15 mai suna Adamu Ibrahim bisa zargin datse hannun wani manomi.

Rahotanni sun nuna cewa wanda ake zargin ya kai hari ne a lokacin da ake fafatawa kan kutsawa cikin gonakin mutane.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Rundunar ‘yan sandan yankin sun kama wani mutum mai suna Adamu Ibrahim da ke kauyen Jital da ke kan titin Gombe a jihar Bauchi, bisa laifin yin zagon kasa, barna da kuma haddasa munanan raunuka.

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...