Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Shugaban Ƙaramar Hukuma A Jihar Nasarawa

Yan bindiga sun sace,Mr. Safiyanu Andaha shugaban karamar hukumar Akwanga ta jihar Nasarawa.

A cewar rahotanni yan bindigar sun sace shugaban karamar hukumar tare da wasu mutane ciki har da wani fitaccen mutum mai taimakon jama’a, Adamu umar wanda aka fi sani da Macciɗo.

Wakilin jaridar Daily Trust ya rawaito cewa shugaban karamar hukumar da sauran mutanen an yi garkuwa da su ne akan titin Andaha-Akwanga da yammacin ranar Litinin.

Wani makusancin shugaban karamar hukumar ya faɗawa jaridar cewa yan bindigar sun fito ne daga cikin daji suka kuma awon gaba da mutanen ya zuwa wani guri da ba asan ko ina ne ba.

Har ya zuwa lokacin wallafa wannan rahoton rundunar yan sandan jihar Nasarawa bata fitar da wata sanarwa ba kan faruwar lamarin.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...