
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya ayyana sunan, Sanata Aliyu Wadada a matsayin wanda yake so ya tsayawa jam’iyar APC takara a zaben shekarar 2027.
Gwamna Sule ya bayyana haka ne a wurin wani taro da ya gudanar tare da masu rike da mukaman siyasa a gidan gwamnatin jihar dake birnin Lafia a ranar Alhamis.
Ayyanawar da gwamnan ya yi wani babban sauyi ne da aka samu a siyasar jihar game da takarar kujerar gwamnan da tuni jiga-jigan Æ´an siyasa da dama suka nuna sha’awarsu ta shiga a dama da su a zaÉ“en 2027.
Wadada shi ne ke wakiltar mazaÉ“ar Kudancin Nasarawa a majalisar dattawa ta Najeriya. A yan kwanakin da suka wuce ne ya sauya sheka ya zuwa jam’iyyar APC daga jam’iyar SDP dai-dai lokacin da ake raÉ—e-raÉ—in cewa zai tsaya takarar gwamnan jihar.

