An Hallaka Mutum 1 A Rikicin Magoya Bayan ’Yan Takarar Gwamnan Nasarawa



Mutum guda ya rasa ransa sakamakon rikici da ya ɓarke tsakanin magoya bayan masu neman takarar gwamnan Jihar Nasarawa a jam’iyyar APC a unguwar Tudun Gwandara da ke Lafiya.

Rahotanni sun ce mamacin mai suna Abbas Rabiu ya samu munanan raunuka a kai yayin rikicin, kafin daga bisani ya rasu a Asibitin Koyarwa na Gwagwalada inda ake yi masa magani.

Mataimaki na Musamman ga Gwamnan Jihar Nasarawa kan harkokin siyasa, Adamu Musa Alƙali, ya ce rikicin ya faru ne yayin wani taron goyon bayan Sanata Wadada, inda ya zargi wasu magoya bayan tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Mohammed Adamu, da kawo hari wurin taron.

Sai dai wani magoyin bayan Mohammed Adamu mai suna Jibrin Ali Baggio ya musanta zargin, yana cewa rikicin ya fara ne bayan wasu mutane sun zo gudanar da wani taro a ƙofar gidan Ɗan’iya Sambo ba tare da amincewa ba.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, SP Ramhan Nansel, ya ce rundunar ba ta samu rahoton lamarin ba zuwa lokacin da aka tuntube shi.

Shi ma Kakakin NSCDC a jihar, Jerry Victor, ya tabbatar da cewa jami’ansu sun isa wurin domin dawo da zaman lafiya.

More from this stream

Recomended