Ƴan bindiga sun sace wasu ɗalibai a jihar Delta

Rahotanni na cewa ƴan bindiga sun sace dalibai da kawo yanzu ba a san yawan adadinsu ba akan babbar hanyar east-west a ƙaramar hukumar Ughelli ta jihar Delta..

A cewar jaridar The Cable ɗaliban dake cikin mota ƙirar Sienna na kan hanyarsu ta dawowa daga birnin Calabar ne  na jihar Cross River lokacin da aka farma motar ta su da yammacin ranar Juma’a.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Delta,Bright Edafe shi  ne ya tabbatarwa da jaridar faruwar haka a ranar Litinin.

Edafe ya ce jami’an ƴan sanda na bin sawun masu garkuwar domin kuɓutar da ɗaliban.

Lamarin ya shiga jerin ƙarin yawan ɗaliban da aka yi garkuwa da su a Najeriya.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...