Ƴan bindiga sun sace wa da ƙane a Zariya

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da yin garkuwa da wani ma’aikacin lafiya tare da dan uwansa a daren Juma’a a unguwar Wusasa da ke karamar hukumar Zariya a jihar Kaduna.

‘Yan bindigar sun kai farmaki yankin ne da misalin karfe 9 na dare inda suka yi ta harbe-harbe don tarwatsa jama’a kafin su dauko wadanda suka kama, Yushau Peter na Asibitin St. Luke Wusasa da dan uwansa, Joshua Peter.

Hakimin kauyen Wusasa Injiniya Isiyaku Ibrahim ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya koka da cewa, “Masu garkuwa da mutane sun sha mayar da yankinmu inda suke kai hare-hare, tare da yin garkuwa da da dama daga cikin mutanenmu.

Ya kara da cewa a unguwar Wusasa da ke wajen tsohon birnin Zazzau, an sha fama da hare-hare a ‘yan kwanakin nan, inda ya ce ba da dadewa ba ne aka kashe wani jami’in soji da dan banga.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...