Ƴan Bindiga Sun Hallaka Mutum 29 a Kaduna

Akalla mutane 29 ne aka kashe a wani sabon hari da wasu ‘yan bindiga suka kai kauyen Runji da ke karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna.

Harin wanda ya faru da misalin karfe 10 na daren ranar Asabar na zuwa ne kwanaki uku bayan wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane takwas a kauyen Atak’Njei da ke karamar hukumar Zangon Kataf.

Kwamishinan tsaron cikin gida da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan wanda ya tabbatar da faruwar sabon lamarin a wata sanarwa da ya fitar, ya ce an kona gidaje da dama a cikin al’ummar yankin yayin da wasu maharan suka jikkata.

Ya kuma bayyana cewa dakarun sojin Najeriya sun yi mumunar arangama da ‘yan bindigar kuma suna nan a yankin gaba daya domin tabbatar da doka da oda.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]