‘Yan sanda sun cafke ‘yan bindiga 30

Rundunar Yan sandan Najeriya ta ce zaratan dakarunta sun cafke wasu gungun yan bindiga dadi kimanin su talatin da takwas.

Da yake nunawa yan jaridu gungun yan bindigar a Abuja, kakakin Rundunar Yan sandan kasar DCP Frank Mba, ya ce an kame yan bindigar ne a sassan arewa maso yamma, arewa maso gabas da arewa ta tsakiya.

An dai kwato manyan bindigogi kirar AK47 guda ashirin da hudu, harsasai Dubu shida da kuma wasu Karin bindigogi kirar gida guda goma sha biyar. Kana da wasu kananan bindigogi kirar Pistols na kwarai. Guda ashirin.

Wannan nasara dai da Yan sandan suka cimma yazo daidai lokacin da yankin arewacin Najeriyar ke ci gaba da fuskantar matsalar tabarbarewar tsaro

Masanin tsaro wing commander musa isa salman Wanda yace wannan nasara na Yansanda na karfafa gwiwa ya nemi da suke kuma bada karfi wajen tattaro bayanan sirri don Kara cimma nasara.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...