Yan fashin daji sun yi garkuwa da wasu iyalai su 7 tare da jikkata ƴan sanda 2 a Abuja

Yan sanda biyu sun samu raunin harbin bindiga a yayin da aka yi garkuwa da wasu iyalai su 7 dai-dai lokacin da yan fashin daji ke cigaba da zafafa kai farmaki a karamar hukumar Bwari dake birnin tarayya Abuja.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa wani mutum mai matsakaicin shekaru da ake kira Alhaji wanda ya yi wa ƴan sandan jagora a ƙoƙarin daƙile yin garkuwa da iyalan ya mutu sakamakon harbin bindiga.

A cewar jaridar a ƴan kwanakin nan yan fashin daji na yawan kai farmaki kauyukan dake karkashin karamar hukumar Bwari inda suke sace mutane tare da kashe wasu.

Wani mazaunin Bwari mai suna Isiah Samuel ya fadawa wakilin jaridar cewa lamarin ya faru da tsakar daren ranar Laraba lokacin yan fashin dajin suka farma unguwar Zuma 1 dake mazabar tsakiyar Bwari.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...